Za A Koma Rubuta Kowace Jarrabawa A Kan Kwamfuta A Nijeriya – Minista

Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta ƙudiri aniyar kawo ƙarshen rubuta kowace jarrabawa a kan takarda, inda ta ce za ta sauya zuwa rubutawa a kan na'urar kwamfuta daga shekarar 2027. 

Ministan Ilimin ƙasar, Dakta Tunji Alausa ne ya bayyana hakan yayin bikin ƙaddamar da kwamitin kyautata ingancin jarrabawa a Nijeriya, wanda aka gudanar a ranar Alhamis a Abuja. 

Alausa ya ce an ɗora wa kwamitin alhakin shawo kan manyan matsalolin da ɓangaren ilimi yake fuskanta a ƙasar, tare da daidaita ayyukan jarrabawa, da kuma tabbatar da gaskiya da inganci. 

Ministan ya kuma jaddada ƙoƙarin gwamantin wajen magance satar amsa da ta yi yawa da kuma ƙarfafa ingancin jarrabawar ƙasar baki ɗaya. 

A dangane da jawabinsa, magance satar amsa yana buƙatar mataki mai tsauri domin ba ɗalibai ba ne kawai suke aikata laifin satar amsar ba. 

Ministan ya ce iyaye ma suna bayar da gudunmawarsu ta hanyar goya wa yaransu baya su yi satar amsar. 

Ya kuma ce malaman makaranta, da shugabannin makaranta, da ma masu kula da jarrabawar suna da hannu a cikin yaɗuwar satar amsa a ƙasar.

Next Post Previous Post
No Comment
Add Comment
comment url
sr7themes.eu.org

Telegram

Instagram

WhatsApp

TikTok

Contact